Home AFIRKA Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun yi kira ga al’ummar ƙasar su kasance a faɗake bayan da wasu koguna suka cika maƙil har su ke barazanar tumbatsa, a yayin da kasar ke ƙoƙarin murmurewa daga ambaliyar da ta kashe mutane sama da ɗari 5 kwanakin baya.

Fira minista, Allamaye Alina ya ce ruwan kogin Chari ya ƙaru da sama da mita 8, kwatankwacin ƙafa 26 a cikin kwanaki 10 da suka gabata.

Babban birnin Chadi, N’Djamena,  yana kusa ne da inda kogunan Logon da Chari suka yi magama, kuma dukannin kogunan sun cika sakamakoln mamakon ruwan sama da ake ta yi.

Tun a watan Yuli ƙasar ta fuskanci mummunar ambaliya, wadda ta lalata gidaje dubu dari da 64 da kadada dubu ɗari 2 da 50 na filayen noma.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp