Home AFIRKA Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun ja hankalin al’umma sakamakon cikar wasu koguna

Mahukuntan Chadi sun yi kira ga al’ummar ƙasar su kasance a faɗake bayan da wasu koguna suka cika maƙil har su ke barazanar tumbatsa, a yayin da kasar ke ƙoƙarin murmurewa daga ambaliyar da ta kashe mutane sama da ɗari 5 kwanakin baya.

Fira minista, Allamaye Alina ya ce ruwan kogin Chari ya ƙaru da sama da mita 8, kwatankwacin ƙafa 26 a cikin kwanaki 10 da suka gabata.

Babban birnin Chadi, N’Djamena,  yana kusa ne da inda kogunan Logon da Chari suka yi magama, kuma dukannin kogunan sun cika sakamakoln mamakon ruwan sama da ake ta yi.

Tun a watan Yuli ƙasar ta fuskanci mummunar ambaliya, wadda ta lalata gidaje dubu dari da 64 da kadada dubu ɗari 2 da 50 na filayen noma.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp