Home AFIRKA Mahukuntan Chadi sun sabunta gargaɗi kan yiwuwar sake fuskantar ambaliya

Mahukuntan Chadi sun sabunta gargaɗi kan yiwuwar sake fuskantar ambaliya

Mahukuntan Chadi sun fitar da sanarwar gargaɗi da ke buƙatar jama’a su ɗauki matakan kariya da kuma yin taka-tsan-tsan don kaucewa asarar rayuka bayan ambaliyar da ta sake kunno kai a tsakar birnin N’Djamena sakamakon mamakon ruwan sama da kuma tumbatsar kogin Chari.

A ɓangare guda bayanai sun ce kogin Logone ya yi tumbatsa mafi ƙololuwa da ba a ga irinta cikin shekaru 30 zuwa 40 da suka gabata ba, wanda ya sanya matakin da ya sanya fargabar sake tsanantar ambaliyar ƙasar wadda kawo yanzu ta hallaka mutane 576 tare da raba wasu miliyan 1 da dubu 900 da matsugunansu tun bayan farowarta a watan Yulin da ya gabata.

Masana sun yi gargaɗin cewa wasu sassa na Chadi ka iya fuskantar zabtarewar laka ƙari kan ambaliyar da ake ci gaba da gani tsawon makwanni.

Ƙasashe da dama a yankunan yammaci da tsakiyar Afrika ne suka yi fam ada ambaliyar ruwa a damunar bana, sai dai halin da ake ciki a Chadi ya fi ko’ina tsananta lura da yadda matsalar ta shafi miliyoyin iyalai.

Shugabar hukumar kula da albarkatun ruwa ta Chadi Sakine Youssouf ta ce tumbatsar kogin Logone ya wuce yadda ake tsammani inda a jiya Laraba ya kai mita 8.18 fiye da yadda aka yi tsammanin tumbatsar shi.

Tuni dai Firaminista Maye Halina ya jagoranci wani taron gaggawa na masu ruwa da tsaki don ɗaukar matakan da za su baiwa jama’a kariya daga ƙaƙƙarfar ambaliyar da ake hasashe da kuma wadda tuni ta shafi yankuna 17 cikin 23 da ƙasar ke da su ciki har da fadar gwamnati.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp