Home AFIRKA Faye ya ƙaddamar da shiri mai dogon zango dan ciyar da Senegal...

Faye ya ƙaddamar da shiri mai dogon zango dan ciyar da Senegal gaba

Gwamnatin Senegal ta ƙaddamar da shirinta mai nisan zango na ciyar da ƙasar gaba, wanda take fatan za a kammala aiwatar da shi cikin shekaru 25 masu zuwa.

Sai dai gwamnatin Senegal ɗin ta bayyana wasu daga cikin muradun da tsara cim-musu cikin shekaru 5.

Muhimman muradun da take fatan cim-musu a gejeren zango kuwa, sun haɗa da rage nauyin bashin da ke kan ƙasar daga kaso 83.7 zuwa kaso 70 cikin 100.

Sai kuma rage giɓin kasafin kuɗi zuwa kashi 3 nan gaba kaɗan, saɓanin giɓin kashi 10.4 da ƙididdiga ta nuna cewar gwa,natin senegal din ta yi fama da shi daga shekarar 2019 zuwa 2023.

Ƙalubale na gaba da gwamnatin Senegal ta sha alwashin magancewa shi ne matsin rayuwa, inda ta yi alƙawarin cikin shekaru biyar da ke tafe, za ta ƙara yawan matsakaicin albashin da ‘yan ƙasar ke samu da kashi 50 cikin 100, kwatankwacin ƙarin daga dala dubu 1, 660 zuwa aƙalla dala dubu 2,648, yayin da kuma za a rage hauhawar farashin kayayyaki zuwa kashi 2 cikin shekaru 5.

Shugaban Senegal Basirou Diomaye Faye da Fira Ministansa Ousmane Sonko ne suka jagoranci kaddamar da gagarumin shirin a garin Diamniadio, mai nisan kilomita 30 daga Dakar babban birnin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp