Home General Gwamna Yusuf ya biya biliyan 16 ga yan fansho a Kano

Gwamna Yusuf ya biya biliyan 16 ga yan fansho a Kano

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatinsa na cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu domin inganta jin dadi da walwalarsu.

” Gwamnatinmu ta damu da walwalarku shi yasa tun da na zo nake cigaba da biyan wadanda suka kammala aiki hakkokinsu, wanda a yau na kaddamar da kashi na uku na biyanku kudaden gama Aiki wato Gratuity”.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria.

Ya ce daga daga hawan gwamnan Yusuf Kan karagar mulki ya biya kimanin naira Biliyan 16 ga yan fansho wanda ya ce hakan zai kara inganta jin dadi da walwalarsu da ma cigaban tattalin arzikin jihar Kano.

” Karon farko na ware biliyan 6 domin biyan wadanda suka gama aiki daga matakin albashi na 10 zuwa kasa, yayin da a kashi na biyu muka biya biliyan 5 ga wadanda suka kammala aiki sakamakon cika shekaru 35″. Inji Abba Kabir

Sanarwar ta kara da cewa gwamna Yusuf ya yi alkawarin cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu, inda yace bai dace a bar su haka ba, idan aka yi la’akari da irin gudunmawar da suka bayar don cigaban jihar Kano a lokacin da suke aiki.

Ya ce zai cigaba da biyan yan fansho hakkokinsu ba tare da bata lokaci ba, inda ya ba su tabbacin za kuma a cigaba da biyansu kudinsu na wata-wata ba tare da wata matsala ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mabiya Addinai Biyu a Najeriya Sun Sanya Hannu Kan Sabuwar YarjejeniyaAn Kashe Matashi Kan Murfin Tayar Adaidaita Sahu a KanoMutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga Sojoji
X whatsapp