Home Labarai Ambaliyar ruwa ta yiwa wasu jihohin Arewa barna

Ambaliyar ruwa ta yiwa wasu jihohin Arewa barna

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da wuraren ibada a jihohin Bauchi da Filato da kuma jihar Neja, lamarin da ya tilasta wa ɗaruruwan mutane barin gidajensu.

Mazauna yankunan da lamarin ya faru sun ce ruwan saman da aka samu kamar da bakin ƙwarya haɗe da iska a wayewar garin ranar Lahadi, ya kayar da bishiyoyi tare da tsige turakun lantarki da ɗaye kwanukan rufi lamarin da ya sa gine-gine da dama suka faɗi.

akalla gine-gine 50 ne suka rushe sakamakon ambaliyar a garin Menkaat na ƙaramar hukumar Shendam a jihar filato.

Can a ƙaramar hukumar Dass ta jihar Bauchi fiye da magidanta 40 suka rasa muhallansu sakamakon ambaliyar da ta lalata gonaki masu yawa a cewar Jaridar.

Haka a jihar Neja kusan garuruwa 18 ne suka fuskanci ambaliyar a ƙaramar hukumar Lapai ta jihar Neja, inda ruwa ya cinye gonaki masu yawa.

Lamarin na zuwa ne dai a daidai lokacin da hukumar hasashen yanayi ta ƙasar, (Nimet) ke gargaɗin samun ruwan sama haɗe da tsawa da yiwuwar samun ambaliya a wasu jihohin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp