Home AFIRKA Shalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kai

Shalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kai

Shalkwatar tsaron Najeriya ta yi ƙarin haske kan kalaman da babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ya yi kan batun kare kai daga hare-haren ƴan fashin daji.

Cikin wata sanarwa da shalkwatar tsaron ta fitar ta ce kalaman Janar Musa ba suna ƙarfafa wa mutane mallakar makami ba ne, kamar yadda wasu kafofin labarai a ƙasar ke yaɗawa.

”Abin da yake nufi shi ne ƴan ƙasa su koyi dabarun kare kai da duniya ta amince da su kamar ƙwarewar tuƙi, da judo da ninƙaya da dambe ko kokawa da sauransu”, in ji sanarwar.

‘Kalamansa ba sa nufin mallakar makami ta haramtacciyar hanya, saboda yana sane da dokokin Najeriya da suka haramta mallakar makami”.

A ranar Alhamis ne cikin wata hira da gidan Talbijin an Channels, Janar Musa ya ce ya kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarun kare kai domin kauce wa hare-haren ƴanbindiga.

Kalaman babban hafsan dai sun janyo ce-ce-ku-ce tsakanin ƴan ƙasar inda wasu ke ganin hakan na nuna gazawa a ɓangaren gwamnati na magance matsalar rashin tsaron da ta ƙi ci ta ƙi cinyewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp