Home General Majalisar dattijai ta amince da kudirin dokar zaɓen da aka yi wa...

Majalisar dattijai ta amince da kudirin dokar zaɓen da aka yi wa gyaran fuska

Majalisar dattijan Najeriya ta zartar da dokar zaɓe da aka yi wa garambawul.

An zartar da ƙudurin dokar ne bayan nazari da amincewa da sassa 155 da ke ƙunshe a cikin ta.

Ɗaya daga cikin gyare-gyaren da aka yi wa dokar ta 2022 shi ne rage wa’adin da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ke da shi na futar da sanarwar zaɓe daga 360 zuwa kwana 180.

Hakan ya biyo bayan amincewa da ƙudirin da Sanata Tahir Monguno ya gabatar na rage kwanakin da ake buƙatar hukumar INEC ta fitar da sanarwar zaɓe.

Monguno ya bayyana cewa rage wa’adin kwanakin ya zama dole domin hukumar INEC ta cika sharuɗɗan da ake buƙata wajen fitar da sanarwar, inda ya ce tuni aka makara idan aka yi amfani da kwana 360 bisa la’akari da babban zaɓe mai zuwa.

Majalisar dai ta fuskanci matsin lamba kan abin da wasu suka bayyana a matsayin jan ƙafa wurin amincewa da ƙudirin dokar zaɓen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp