Home Labarai Nijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyu

Nijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyu

Jamhuriyar Nijar ta amince da kundin ayyukan Ƙungiyar Kasashen Sahel (AES) na shekara ta biyu wadda ta haɗa da Mali da Burkina Faso, kafin taron ministoci da za a gudanar a Ouagadougou daga 24 zuwa 26 ga watan Fabrairu, kamar yadda jaridar gwamnati ta ANP ta ruwaito a ranar 21 ga Fabrairu.

Firaminista Ali Mahamane Lamine Zeine ya gana da ministoci da mambobin kwamitin ƙasa na AES a ranar 21 ga Fabrairu domin daidaita matsayi kafin taron yankin.

Mataimakiyar Shugabar kwamitin, Bayard Mariama Gamatie, ta ce Burkina Faso ta raba wani kundin aiki, wanda Nijar ta gyara bisa ginshiƙai uku da suka haɗa da tsaro da diflomasiyya, ci gaban ƙasa, da tsaro da kare iyaka.

“An amince da kundin gaba ɗaya, dangane da shawarwarin gyare-gyaren Nijar,” in ji Gamatie.

Rahoton ya nuna cewa ministocin Nijar sun duba kundin sun kuma yi gyare-gyare da sake fasalta wasu abubuwa, sannan sun bayar da shawarwari don taron ƙwararru da zai biyo baya.

An kafa AES a shekarar 2023, bayan da ƙasashen uku suka janye daga Ƙungiyar ECOWAS, domin tsara manufofi na tsaro da diflomasiyya, da ci gaban ƙasa tsakanin ƙasashen Sahel.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp