Home SIYASA 2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

Atiku

2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara – Atiku

 

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar, ya ce ba zai sake neman takarar shugaban ƙasar daga 2027 ba.

Ya ce idan aka yi la’akari da shekarunsa da kuma damar da yake da ita ba lallai ya ci gaba da neman damar daga shekara mai zuwa ba.

Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a ranar Laraba.

Da aka tambaye shi game da cikarsa shekaru 80 a shekarar 2027 da yadda hakan zai iya daƙile masa damarsa, Atiku ya ce: “Tabbas za a samu ƙarin masu nema, kuma ita ce dama ta ƙarshe da zan fito takarar”

Atiku ya yi takarar shugaban ƙasar a lokuta da dama.

Ya nemi tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 1993 a karkashin jam’iyyar SDP inda daga baya ya bar wa Moshood Abiola, da kuma Action Congress a shekarar 2007, inda marigayi Umaru Musa Yar’Adua ya lashe zaɓen.

Atiku ya kuma tsaya takara a shekarar 2011 karkashin jam’iyyar ACN, inda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.

Ya koma jam’iyyar PDP ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2019, inda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

A 2023, ya sake fitowa takarar a PDP amma ya sha kaye a hannun Shugaba Bola Tinubu na APC.

 

 

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp