Home SIYASA Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

Momodu

Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

 

Abuja – Daya daga cikin manya a jam’iyyar ADC, Dele Momodu, ya yi magana game da zaben shugaban kasa na 2027 a Najeriya.

Dele Momodu ya bayyana cewa Peter Obi ya taba kin amincewa da shawararsa ta hada kai da Atiku Abubakar a siyasa.

Abin da Obi ya fada kan Atiku Abubakar

Momodu ya ce Obi ya shaida masa cewa ya fi Atiku farin jini a tsakanin al’umma, cewar rahoton Punch.

Tsohon ‘dan takarar shugaban kasar ya bayyana cewa idan aka tambayi Obi, zai tabbatar bai yi masa karya ba ko kadan a kalamansa.

Momodu ya ce:

“Peter shi ne ɗan siyasa kaɗai da ya taɓa ziyartar gidana a London, Ghana da Lagos, a ɗaya daga cikin ziyarar, na gaya wa Peter cewa, ‘Ka yi ƙoƙarin yin aiki tare da Atiku.’

Momodu ya ce ya kawo misalin John Mahama na Ghana, wanda watakila da bai zama shugaban kasa ba da bai fara zama mataimakin Atta Mills ba.

Ya kuma kawo misalin Amurka, inda Joe Biden ya dawo ya zama shugaban kasa bayan ya nuna kwarewa duk da tsufansa.

“Na kuma ba shi misalin Amurka, inda duk da cewa Biden ya fi Obama shekaru sosai, amma daga baya ya dawo ya zama Shugaban Ƙasa saboda ya nuna ƙwarewa da cancantarsa.

“Kai dai ka taɓa zama gwamnan jiha ne kawai, amma Peter ya gaya mini cewa ya fi Atiku farin jini. Na rantse da Ubangiji. Idan ka gan shi, ka tambaye shi ko na yi masa ƙarya.”

A cewarsa, Obi ya taba zama gwamnan jiha ne kawai, amma ya dage yana ikirarin cewa ya fi Atiku karbuwa a idon jama’a, cewar Daily Post.

Momodu ya kuma yi tsokaci kan yanayin siyasar kasar, yana cewa akwai masu ruwa da tsaki da dama da ke fargabar karuwar tasirin Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp