Home SIYASA Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

Momodu

Abin da Obi ya Fada Kan Atiku – Dele Momodu

 

Abuja – Daya daga cikin manya a jam’iyyar ADC, Dele Momodu, ya yi magana game da zaben shugaban kasa na 2027 a Najeriya.

Dele Momodu ya bayyana cewa Peter Obi ya taba kin amincewa da shawararsa ta hada kai da Atiku Abubakar a siyasa.

Abin da Obi ya fada kan Atiku Abubakar

Momodu ya ce Obi ya shaida masa cewa ya fi Atiku farin jini a tsakanin al’umma, cewar rahoton Punch.

Tsohon ‘dan takarar shugaban kasar ya bayyana cewa idan aka tambayi Obi, zai tabbatar bai yi masa karya ba ko kadan a kalamansa.

Momodu ya ce:

“Peter shi ne ɗan siyasa kaɗai da ya taɓa ziyartar gidana a London, Ghana da Lagos, a ɗaya daga cikin ziyarar, na gaya wa Peter cewa, ‘Ka yi ƙoƙarin yin aiki tare da Atiku.’

Momodu ya ce ya kawo misalin John Mahama na Ghana, wanda watakila da bai zama shugaban kasa ba da bai fara zama mataimakin Atta Mills ba.

Ya kuma kawo misalin Amurka, inda Joe Biden ya dawo ya zama shugaban kasa bayan ya nuna kwarewa duk da tsufansa.

“Na kuma ba shi misalin Amurka, inda duk da cewa Biden ya fi Obama shekaru sosai, amma daga baya ya dawo ya zama Shugaban Ƙasa saboda ya nuna ƙwarewa da cancantarsa.

“Kai dai ka taɓa zama gwamnan jiha ne kawai, amma Peter ya gaya mini cewa ya fi Atiku farin jini. Na rantse da Ubangiji. Idan ka gan shi, ka tambaye shi ko na yi masa ƙarya.”

A cewarsa, Obi ya taba zama gwamnan jiha ne kawai, amma ya dage yana ikirarin cewa ya fi Atiku karbuwa a idon jama’a, cewar Daily Post.

Momodu ya kuma yi tsokaci kan yanayin siyasar kasar, yana cewa akwai masu ruwa da tsaki da dama da ke fargabar karuwar tasirin Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp