Home SIYASA PDP ta Mika Sunayen Masu Maye Gurbin Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa

PDP ta Mika Sunayen Masu Maye Gurbin Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa

PDP ta Mika Sunayen Masu Maye Gurbin Gwamnan Jahar Ebonyi da Mataimakinsa

A yau ne kotu a Abuja ta ba da umarnin a tsige gwamnan jihar Ebonyi bayan da ya koma jam’iyyar APC daga PDP.

Tsigewar ta shafi mataimakinsa, wanda tare da mai gidan nasa suka koma APC; jam’iyya mai mulki a Najeriya.

Jam’iyyar PDP ta tura wa INEC sunayen wadanda take son su maye gurbin gwamna Umahi da mataimakinsa.

Jam’iyyar PDP ta ce ta mika sunayen mutanen da ta amince su maye gurbin gwamnan Ebonyi da mataimakinsa ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), TheCable ta ruwaito.

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Talata, ta ba da umarnin tsige gwamnan Ebonyi, Dave Umahi, da mataimakinsa Eric Kelechi Igwe, biyo bayan sauya sheka da suka yi zuwa jam’iyyar APC.

Bayan faruwar lamarin, Shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Iyorchia Ayu, a wani taron manema labarai a ranar Talata, ya ce jam’iyyar ta zabi Iduma Igariwe da Fred Udogwu a madadin Umahi da Igwe domin ci gaba da mulkar jihar.

Wani bidiyon da PDP ta yada a shafinta na Twitter yana dauke da rubutu kamar haka:

“Bayan tsige Gwamna Dave Umahi da Mataimakinsa Mista Igwe na jihar Ebonyi, kuma bisa ga umarnin kotu, PDP ta mika wa INEC sunayen Iduma Igariwe da Fred Udogwu a matsayin sabon Gwamna da kuma mataimakin gwamnan Jihar Ebonyi”

Jam’iyyar APC a jihar Ebonyi, ta ce babu abin da zai kawo wani dan jam’iyyar PDP kusa da kujerar mulkin gwamnan jihar, kamar yadda Vanguard ta ruwaito.

Wannan na daya daga cikin lamurran da suke faruwa a APC tun bayan shillawar shugaban kasa Muhammadu Buhari birnin Landon domin duba lafiyarsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp