Home SIYASA Watan da Za a Fara Kamfe – INEC

Watan da Za a Fara Kamfe – INEC

Watan da Za a Fara Kamfe – INEC

 

Hukumar zabe mai cin gashin kai a Najeriya, INEC ta ce nan da kusan watanni shida za a fara kamfe.

Daga ranar 28 ga watan Satumba za a bada dama domin a fara yakin neman zaben shugaban kasa.

Zuwa Watan Maris 2023 za a rufe kofar kamfe, a jira ranar zaben jihohi, majalisa da shugaban kasa.

Kaduna – A lokacin da aka fara hango hadarin siyasar 2023, hukumar zabe mai zaman kanta watau INEC ta tsaida lokacin da za a soma kamfe a Najeriya.

Jaridar Daily Trust a wani rahoto da ta fitar a ranar Alhamis, ta ce INEC ta sa lokacin da za a fara yakin neman takarar gwamna, majalisa da na shugaban kasa.

Hukumar zabe ta kasa ta ce daga ranar Laraba, 28 ga watan Satumban 2022 za a soma yakin neman zaben shugaban kasa da na kujerun majalisar tarayya.

A wannan lokaci ne masu harin kujerar shugaban kasa da masu neman zama Sanatoci da ‘Yan majalisar wakilan tarayya za su fara kamfe a fadin kasar nan.

INEC ta kuma tsaoda ranar 12 ga watan Oktoban 2022 a matsayin lokacin da za a iya fara yawon yakin neman takarar gwamna da na majalisar dokoki a jihohi.

Babbar kwamishinar zabe ta shiyyar Kaduna, Hajiya Asmau Sani Maikudi ta shaidawa manema labarai wannan a lokacin da ta zanta da su a yammacin Laraba.

Yaushe za a gama kamfe?

Da take jawabi a Kaduna, Asmau Maikudi ta bayyana cewa daga ranar 23 ga watan Fubrairun 2023, an rufe yakin zaben ‘yan majalisa da na shugaban kasa.

Haka zalika bayan 9 ga watan Maris 2023, babu ‘dan takarar gwamna ko ‘dan majalisar dokoki da zai cigaba da kamfe. Za ayi kusan watanni biyar ana yakin zabe.

Ana cigaba da shirin 2023

Rahoton ya kuma tabbatar da cewa hukumar INEC ta kara adadin rumfunan zabe a Najeriya. Daga rumfuna 5012 da aka yi amfani da su a 2019, yanzu akwai 8012.

A jawabin na jami’ar hukumar zaben, an kuma fahimci mutane su na cigaba da yin rajistar samun katin zabe na kasa. A yanzu mutane 236,855 sun fara yin rajista.

Zuwa farkon makon nan, mutane 84,335 ne kurum suka kammala rajistar samun katin kada kuri’ar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp