Home SIYASA Kotun Koli a Najeriya ta Tabbatar da Soke Rajistar Jam’iyyun Siyasa 22

Kotun Koli a Najeriya ta Tabbatar da Soke Rajistar Jam’iyyun Siyasa 22

Kotun Koli a Najeriya ta Tabbatar da Soke Rajistar Jam’iyyun Siyasa 22

Abuja Kotun koli a Najeriya ta tabbatar da hukuncin soke rajistar wasu jam’iyyun siyasa 22 da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi a shekarun baya.

Jam’iyyu 22 na daga cikin 74 da INEC ta soke rajistarsu a 2020 sakamakon rashin tabuka abin a zo a gani a zaben 2019, inji rahoton Leadership.

Mai shari’a Ejembi Eko na kotun koli ya yi watsi da hukuncin da kotun daukaka kara da ke Abuja ta yanke, wanda ya kalubalanci matsayar INEC na soke rajistar jam’iyyun.

Mai shari’a Eko ya bayyana cewa, Kotun daukaka kara a karan kanta ta tabo batun rashin sauraron shari’ar adalci ga bangaren jam’iyyun 22 da aka soke, inda ta cimma matsaya ba tare da jin ta bakin wasu bangarori a kan lamarin ba.

A cewar mai shari’a:

“Wannan bukata da INEC ta nema ya dace kuma an amince da hakan. Hukuncin kotun da ke kasa an yi watsi da shi.”

Kotun kolin ta bayyana cewa kotun daukaka kara ya fitar da batun sauraron karar ne daga duban bukatar daukaka kara da jam’iyyun siyasa suka shigar amma ta ki yin abin da ya dace domin yin adalci ga wasu da lamarin ya shafa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp