Home Taska Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun...

Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun Hijira a Abuja

Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun Hijira a Abuja

A ƙoƙarinta na cimma fata da burin mai girma shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, (GCFR), na fidda ƴan Nageriya kimanin mutum miliyan ɗari daga cikin ƙangin fatara gami da talauci, hukukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), ta ƙaddamar da shirinta na ba da horon ƙwarewa kan fasahar zamani ga ƴan gudun hijira, matafiya, da kuma waɗanda fitintinu su ka raba su da muhallansu.

Horon wanda za a shafe tsawon yini (5) ana gudanar da shi, an ƙaddamar da fara shi ne a yau a cibiyar horar da ma’aikata ilimin aikin gwamnati a zamanance, (E-Government Training Center), da ke yankin Kubuwa, birnin tarayya Abuja, kana haɗin gwiwa ne a tsakanin hukumar ta (NITDA) da kuma hukumar kula da al’amuran ƴan gudun hijira ta tarayyar Nageriya, “National Commission For Refugees Migrants And Internally Displaced Persons (NCFRMI).

Horon da ke da manufar bunƙasa ƙwarewa kan hikimomi da dabarun ilimin fasahar sadarwar zamani domin harkar kasuwanci da sana’o’in dogaro da kai a zamanance, kimanin mutane ɗari biyu ƴan gudun hijira, da masu ƙaura, da waɗanda iftila’i ya raba da muhallansu ne za su amfana a birnin Abuja kafin daga bisani kuma a faɗaɗa shirin zuwa sauran Jihohin Nageriya.

Mai girma shugaban ƙasa Malam Muhammadu Buhari, (GCFR), tuntuni ya yi alƙawarin fidda ƴan Nageriya kimanin mutum (Miliyan 100) daga cikin talauci nan da shekarar (2030) da yardar Allah. Wanda a ƙarƙashin wannan turba hukumar ta (NITDA), da ma’aikatar sadarwa, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), su ka himmatu ka’in da na’in wajen ba wa al’ummar Nageriya daban-daban horo kan hikimomi da dabaru na ilimin fasahar sadarwar zamani domin su samu sana’o’i da kasuwancin dogaro da kai.

Litinin, 14 ga watan Fabarairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp