Home Taska Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun...

Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun Hijira a Abuja

Hukumar NITDA ta Fara ba da Horo ga Mutane 200 Ƴan Gudun Hijira a Abuja

A ƙoƙarinta na cimma fata da burin mai girma shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, (GCFR), na fidda ƴan Nageriya kimanin mutum miliyan ɗari daga cikin ƙangin fatara gami da talauci, hukukumar bunƙasa fasahar sadarwar zamani ta ƙasa, (NITDA), ƙarƙashin jagorancin Malam Kashif Inuwa Abdullahi, (CCIE), ta ƙaddamar da shirinta na ba da horon ƙwarewa kan fasahar zamani ga ƴan gudun hijira, matafiya, da kuma waɗanda fitintinu su ka raba su da muhallansu.

Horon wanda za a shafe tsawon yini (5) ana gudanar da shi, an ƙaddamar da fara shi ne a yau a cibiyar horar da ma’aikata ilimin aikin gwamnati a zamanance, (E-Government Training Center), da ke yankin Kubuwa, birnin tarayya Abuja, kana haɗin gwiwa ne a tsakanin hukumar ta (NITDA) da kuma hukumar kula da al’amuran ƴan gudun hijira ta tarayyar Nageriya, “National Commission For Refugees Migrants And Internally Displaced Persons (NCFRMI).

Horon da ke da manufar bunƙasa ƙwarewa kan hikimomi da dabarun ilimin fasahar sadarwar zamani domin harkar kasuwanci da sana’o’in dogaro da kai a zamanance, kimanin mutane ɗari biyu ƴan gudun hijira, da masu ƙaura, da waɗanda iftila’i ya raba da muhallansu ne za su amfana a birnin Abuja kafin daga bisani kuma a faɗaɗa shirin zuwa sauran Jihohin Nageriya.

Mai girma shugaban ƙasa Malam Muhammadu Buhari, (GCFR), tuntuni ya yi alƙawarin fidda ƴan Nageriya kimanin mutum (Miliyan 100) daga cikin talauci nan da shekarar (2030) da yardar Allah. Wanda a ƙarƙashin wannan turba hukumar ta (NITDA), da ma’aikatar sadarwa, ƙarƙashin jagorancin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami, (FNCS, FBCS, FIIM), su ka himmatu ka’in da na’in wajen ba wa al’ummar Nageriya daban-daban horo kan hikimomi da dabaru na ilimin fasahar sadarwar zamani domin su samu sana’o’i da kasuwancin dogaro da kai.

Litinin, 14 ga watan Fabarairu, 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp