Home SIYASA An Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo

An Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo

Jagoran jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, kuma Dan Takarar Shugabancin Qasa karkashin Inuwar Jam’iyyar, Bola Ahmad Tinubu yace Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo ba Dan sa bane.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai a yammacin ranar Litinin a Birnin Tarayya Abuja, jim kadan bayan kammala ganawar sa da Gwamnonin Jam’iyyar APC su 12.

Ganawar da aka yi a masaukin Gwamnan Jihar Kebbi, a Asokoro dake Birnin tarayya Abuja, ta zo bayan Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osibanjo ya bayyana Kudirin sa na tsayawa takarar Shugaban Kasa a kakar zaben shekarar 2023.

Da aka tambaye shi don yin tsokaci dangane da Takarar Mataimakin Shugaban Kasar, wanda ake masa kallon dansa ne a siyasance, Tinubu yace “Bani da wani da da ya girma da zai iya yin Takarar shugaban kasa, “Bani da wani Da daya girma zai iya wannan furuci.

Sai dai yace ya ganawa da gwamnonin jihohin ne domin neman hadin kai, goyon baya da karfafa Gwuiwa dangane da burin sa na tsayawa takarar shugabancin Nijeriya a shekarar 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp