An Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo

Jagoran jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, kuma Dan Takarar Shugabancin Qasa karkashin Inuwar Jam’iyyar, Bola Ahmad Tinubu yace Mataimakin Shugaban Kasa Farfesa Yemi Osibanjo ba Dan sa bane.

Ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai a yammacin ranar Litinin a Birnin Tarayya Abuja, jim kadan bayan kammala ganawar sa da Gwamnonin Jam’iyyar APC su 12.

Ganawar da aka yi a masaukin Gwamnan Jihar Kebbi, a Asokoro dake Birnin tarayya Abuja, ta zo bayan Mataimakin Shugaban Kasa Yemi Osibanjo ya bayyana Kudirin sa na tsayawa takarar Shugaban Kasa a kakar zaben shekarar 2023.

Da aka tambaye shi don yin tsokaci dangane da Takarar Mataimakin Shugaban Kasar, wanda ake masa kallon dansa ne a siyasance, Tinubu yace “Bani da wani da da ya girma da zai iya yin Takarar shugaban kasa, “Bani da wani Da daya girma zai iya wannan furuci.

Sai dai yace ya ganawa da gwamnonin jihohin ne domin neman hadin kai, goyon baya da karfafa Gwuiwa dangane da burin sa na tsayawa takarar shugabancin Nijeriya a shekarar 2023.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 13 minutes 54 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 55 minutes 19 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com