• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Taska Fusatattun Matasa sun Kai Hari a Matsugunin Fulani
  • Taska

Fusatattun Matasa sun Kai Hari a Matsugunin Fulani

By
Prnigeria
-
April 11, 2022
Arewa Award

Fusatattun Matasa sun Kai Hari a Matsugunin Fulani

‘Yan bindiga da ba’a san ko suwaye ba sun hallaka sabon shugaban Al’ummar Kakura dake Karamar Hukumar Chikun ta jihar Kaduna a ranar Lahadi Isiaku Madaki.

Jaridar Emergency Digest ta rawaito Wani mazaunin yankin Baban David ya bayyana cewa an nada marigayin matsayin shugaban Al’ummar ne a ranar Asabar.

“Mun taru a gidansa da sanyin safiyar ranar ta Asabar domin taya shi murnar nadin da aka yi masa, amma munyi mamakin yadda muka fara jin karara harbe-harbe a safiyar ranar Lahadi.

“Karar habin ta razana mu matuka, domin yadda muka ji karar ta hana mu fitowa daga gidajen mu, sai dai daga bisani aka fada mana ‘Yan Bindigar sun halaka shi a gaban matar sa da ‘Ya’yan sa.

Read Also:

  • Bama goyan bayan ayyukan ta’addanci a Najeriya – Miyetti Allah
  • Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina
  • Shalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kai

“Mun sami gawar sa yashe akar; Matar sa ta fada mana ‘Yan Bindigar sun karya kofar gidan suka kuma hallaka mijin nata ta hanyar harbi, amma dai basu dauki komai ba, kuma ba suyi garkuwa da kowa ba.

Sai dai wani rahoto ya bayyana cewa a safiyar wannan rana, wasu fusatattun matasa sun kai hari a matsugunin Fulani inda ake fargabar mutuwar mutane 14.

Wani bafullatani dake zaune a yankin, Malam Buhari ya bayyana cewa, ‘Yan Asalin yankin sun kewaye matsugunan su inda suke cewa su bar musu yankin tunda sun fara munafurtar su.

Ya kara da cewa yayin da suke fita daga yankin an kai musu farmaki tare da kashe wasu daga cikin su, yana mai cewa “ akan hanyarmu ta zuwa kauyen mun kirga gawarwaki hudu, daga bisani kuma a cikin daji mun kirga gawarwaki wasu mutum 10.

A yayin hada wannan rahoton an tura ‘yan sanda zuwa garin domin maido da zaman lafiya, duk da cewa yanzu haka Al-amura sun fara komawa yadda suke a baya, duk da cewa akasarin mutane yankin sun tsere saboda fargaba.

Sai dai kawo yanzu rundunar ‘yan sandan jihar, da gwamnatin jihar basu ce komai ba dangane da lamarin.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • 'yan bindiga
  • Emergency Digest
  • Fulani
  • kaduna
Previous articleAn Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo
Next article‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39 da Hannun ‘Yan Bindiga
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Azumin Bara: Talge Muka Riƙa Sha a Hannun Maharan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

Magance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

An Gudanar Da Bikin Arewa Stars 30 Under 30 2022, Cikin Nasara

Manomi Yayiwa Wata Mata Yankan Rago

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Gidauniyar Malam Inuwa Da Kokarinta Na Ilmantar Da Mutanen Karkara Da Rugage

Gidauniyar Malam Inuwa ta Ɗauki Nauyin Koyar da Ƴa’yan Fulani Al-ƙur’ani

Bincike: Shin Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ƙirƙiro da Tambayoyi Domin Tantance kungiyoyin Musulmi da Kirista a kidayar 2023? 

Recent Posts

  • Bama goyan bayan ayyukan ta’addanci a Najeriya – Miyetti Allah
  • Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina
  • Shalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kai
  • Gwamnonin PDP na taro a Zamfara
  • Ya kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarar kare kai – Musa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1529 days 11 hours 43 minutes 27 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1511 days 13 hours 24 minutes 52 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Bama goyan bayan ayyukan ta'addanci a Najeriya - Miyetti AllahSojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a KatsinaShalkwatar tsaron Nijeriya ta yi karin bayani kan batun kare kaiGwamnonin PDP na taro a ZamfaraYa kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarar kare kai - MusaHukumar KAROTA ta kaddamar da kotun tafi da gidanka a jihar Kanokotu ta dakatar da asusun banki huɗu na Mele KyariAna neman mutane 40 a cikin Kogi bayan kifewar kwale-kwale a SokotoA biya mu haƙƙoƙinmu, ba mu son bashin gwamnati - ASUUAmurka za ta sayar wa Nijeriya makamai da kuɗinsu ya kai dala miliyan 346PDP za ta ƙaddamar da kwamitocin zartaswa na shiyoyiEFCC ta ba da belin tsohon gwamnan Sokoto Tambuwal da ta tsareMajalisar Dokokin Kano ta Dakatar da Ciyaman din RanoƘananan dillalan mai sun zargi shugabanninsu da yiwa Matatar Dangote zagon ƙasaAtiku Abubakar ya magantu kan tsare Tambuwal da EFCC ta yi
X whatsapp