• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home Taska Fusatattun Matasa sun Kai Hari a Matsugunin Fulani
  • Taska

Fusatattun Matasa sun Kai Hari a Matsugunin Fulani

By
Prnigeria
-
April 11, 2022
Arewa Award

Fusatattun Matasa sun Kai Hari a Matsugunin Fulani

‘Yan bindiga da ba’a san ko suwaye ba sun hallaka sabon shugaban Al’ummar Kakura dake Karamar Hukumar Chikun ta jihar Kaduna a ranar Lahadi Isiaku Madaki.

Jaridar Emergency Digest ta rawaito Wani mazaunin yankin Baban David ya bayyana cewa an nada marigayin matsayin shugaban Al’ummar ne a ranar Asabar.

“Mun taru a gidansa da sanyin safiyar ranar ta Asabar domin taya shi murnar nadin da aka yi masa, amma munyi mamakin yadda muka fara jin karara harbe-harbe a safiyar ranar Lahadi.

“Karar habin ta razana mu matuka, domin yadda muka ji karar ta hana mu fitowa daga gidajen mu, sai dai daga bisani aka fada mana ‘Yan Bindigar sun halaka shi a gaban matar sa da ‘Ya’yan sa.

Read Also:

  • Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawa
  • Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya
  • Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri

“Mun sami gawar sa yashe akar; Matar sa ta fada mana ‘Yan Bindigar sun karya kofar gidan suka kuma hallaka mijin nata ta hanyar harbi, amma dai basu dauki komai ba, kuma ba suyi garkuwa da kowa ba.

Sai dai wani rahoto ya bayyana cewa a safiyar wannan rana, wasu fusatattun matasa sun kai hari a matsugunin Fulani inda ake fargabar mutuwar mutane 14.

Wani bafullatani dake zaune a yankin, Malam Buhari ya bayyana cewa, ‘Yan Asalin yankin sun kewaye matsugunan su inda suke cewa su bar musu yankin tunda sun fara munafurtar su.

Ya kara da cewa yayin da suke fita daga yankin an kai musu farmaki tare da kashe wasu daga cikin su, yana mai cewa “ akan hanyarmu ta zuwa kauyen mun kirga gawarwaki hudu, daga bisani kuma a cikin daji mun kirga gawarwaki wasu mutum 10.

A yayin hada wannan rahoton an tura ‘yan sanda zuwa garin domin maido da zaman lafiya, duk da cewa yanzu haka Al-amura sun fara komawa yadda suke a baya, duk da cewa akasarin mutane yankin sun tsere saboda fargaba.

Sai dai kawo yanzu rundunar ‘yan sandan jihar, da gwamnatin jihar basu ce komai ba dangane da lamarin.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • 'yan bindiga
  • Emergency Digest
  • Fulani
  • kaduna
Previous articleAn Fara Kace Nace Tsakanin Tinubu da Osibanjo
Next article‘Yan Sanda a Jihar Zamfara Sun Sami Nasarar Kubutar da Mutane 39 da Hannun ‘Yan Bindiga
Prnigeria

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Azumin Bara: Talge Muka Riƙa Sha a Hannun Maharan Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna

Zambar N2.2bn: EFCC ta Sake Gurfanar da ɗan Tsohon Shugaban PDP

Magance Karancin Naira: CBN ya Umarci Bankuna da su yi Aiki a Ranakun Asabar da Lahadi

Hatsarin Mota ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 25 a Bauchi

Hukumar NITDA ta Gabatar da Satifiket ga Matan da Suka Samu Horo Kan Fasahar Zamani

Ambaliyar Ruwa a Jigawa: Gidauniyar Ƙasar Qatar da ta Malam Inuwa Sun Raba Tallafin Abinci ga Mutane 1,000

An Gudanar Da Bikin Arewa Stars 30 Under 30 2022, Cikin Nasara

Manomi Yayiwa Wata Mata Yankan Rago

‘Yan Sanda Sun Kama Wadanda Ake Zargi da Kashe ‘Yan Sanda Biyu a Anambra

Gidauniyar Malam Inuwa Da Kokarinta Na Ilmantar Da Mutanen Karkara Da Rugage

Gidauniyar Malam Inuwa ta Ɗauki Nauyin Koyar da Ƴa’yan Fulani Al-ƙur’ani

Bincike: Shin Hukumar Kidaya ta Kasa (NPC) ta ƙirƙiro da Tambayoyi Domin Tantance kungiyoyin Musulmi da Kirista a kidayar 2023? 

Recent Posts

  • Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawa
  • Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya
  • Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri
  • KACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami’anta
  • Dino Melaye ya koma jam’iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1507 days 9 hours 20 minutes 29 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1489 days 11 hours 1 minute 54 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawaTinubu ya yi karin wa'adin Aiki ga shugaban Custom na NijeriyaGini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar MaiduguriKACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami'antaDino Melaye ya koma jam'iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDPMamakon ruwan sama ya haifar da ambaliya a MaiduguriAn samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga - RibaduHadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar JigawaZanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke Kenyazamu hallaka Da;iban da ke hannun mu matukar baku biya Fansa ba - 'Yan BindigaGwamnan Zamfara ya Amince da Nadin Sabon Sarki GusauAkalla jami'an tsaron jihar Katsina 100 suka mutu a bakin aiki - KwamishinaYadda yan bindiga suka yiwa mutane 38 yankan RagoAmbaliyar ruwa ta lalata gidaje tare da kashe mutane 23 da a birnin YolaFadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu
X whatsapp