Masu Garkuwa Da Suka Yi Garkuwa Da Wata Mata A Legas Sun Nemi Fansan Miliyan 10

‘Yan bindigar da sukayi garkuwa da wata mata a garin Legas sun tuntubi ‘yan uwan ta, in da suka bukaci a biya su fansar naira Miliyan 10.

An ruwaito cewa masu garkuwar da su kayi badda bami matsayin masu sayen kaya a babban kantin dake unguwar Plywood ta Epe da misalign karfe 10:07Pm sun bayyana cewa suna bukatar sayen ruwa ne kamar yadda mijinta ya bayyana wanda yace suna tare a kantin.

Sai dai ana tsaka da hada-hadar cinikayya a kantin ne kawai hasken lantarki ya dauki abinda ya kai ga ‘yan bindigar sun amshe wayoyin ma’auratan baya ga lakada musu dukan kawo wuka.

Daga bisani kuma suka rufe mijin matar a kantin suka kuma yi awon gaba da matar da nufin yin garkuwa da ita.

Wani dan uwan wadda aka yi garkuwar da ya nemi a sakaye sunan sa, ya bayyana cewa masu garkuwar sun kira mijin matar inda suka bukaci ya biya naira Miliyan 50 matsayn fansar matar sa.

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta bakin kakakin ta SP Hudenyin ta tabbatar da faruwar lamarin, inda tace tana bincike domin tabbatar da an kubutar da matar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 32 minutes 32 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 13 minutes 57 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com