Ana Fargabar Gini Ya Rufta Kan Mutane Da Dama A Jihar Kano

Rahotanni daga kasuwar sayar da wayoyin hannu dake titin beirut a birnin kano dake Arewacin Nijeriya, na cewa wani bene ya rufta kuma ana tsammanin ya danne mutane da dama.
shaidun gani da ido sun shaidawa wakilan mu cewa, yanzu haka ana cen ana kokarin ceto wadanda ke karkashin baraguzai, yayin da aka garzaya da wadanda suka ji rauni asibiti.
Ko dai a ‘yan tsakanin nan Wani ginin bene mai hawa uku da ake aikin ginisa ya rufta a unguwar Kubwa da ke Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.
Faduwar ginin dai ya rutsa da mutanen bakwai a ciki inda jami’an biyu daga cikinsu suka mutu yayin da jami’an hukumar kai daukin gaggawa ta Abuja suka samu ceto mutane biyar daga baraguzan ginin.
Ba kasafai aka fiya samun ruftawar gini a jihar ba, duk da cewa dai shaidun gani da ido sun dora alhakin rushewar kan rashin ingancin kayan aikin gini.
Kawo yanzu dai hukumomi a jihar basu ce kamai kan wannan lamarin ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 25 minutes 40 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 7 minutes 5 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com