Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

Allah ya yi wa Mai Garin Lokoja Rasuwa

 

LABARIN SIYASA – An bayar da rahoton rasuwar basaraken gargajiyar Lokoja, wanda aka fi sani da Mai Gari na Lokoja, Alhaji Muhammadu Kabiru Makarfi III.

Majiyoyin fadar da dama sun shaidawa SIYASA DIGEST a daren Laraba cewa mai martaba sarkin ya rasu da misalin karfe 4 na yamma.

Wakilinmu ya kuma tattaro cewa basaraken mai shekaru 80 a duniya ya rasu ne a wani asibitin Abuja da ba a bayyana ba.

Mai Gari ya kwashe watanni yana jinya inda aka kai Asibitoci daban-daban a Saudiyya da Masar kafin daga bisani ya kare a Abuja.

Majiyoyin da suka kware a fadar sun kara da cewa za a yi jana’izarsa kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a ranar Alhamis.

Mai Gari ya hau karagar mulki tun 1991. Ya rasu ya bar mata da ‘ya’ya da jikoki.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 21 hours 9 minutes 22 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 50 minutes 47 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com