Al’shabab ta sake kai hari wani Otal a Somalia

Wasu rahotanni na bayyana cewa akalla mutane 3 sun rasa rayukansu, sannan da dama sun jikkata sakamakon wani hari da aka kai da mota makare da bama-bamai da kuma harbe-harben bindiga kan wani otel da ke birnin Kismayu na kasar Somalia.

An fara jin karar harbe-harben bindiga jim kadan da fashewar bama-bamai da ke cikin motar wadda ta  yi karo da babban kofar shiga cikin otel din na Tawakal, yayin da mayakan Al-Shebab masu alaka da Al-Qaeda suka dauki alhakin kaddamar da farmakin.

Rahotanni na cewa, an kai farmakin ne a daidai lokacin da ake kan gudanar da wani taro a otel din kan yadda za a murkushe mayakan na  Al-Sshebab a kasar ta Somalia.

Har yanzu dai kungiyar ta Al-Shebab na rike da ikon wasu yankuna na birnin na Kismayu mai cike da hada-hadar kasuwanci a yankin kudancin Somalia.

Sojojin kasar sun yi nasarar fatattakar mayakan na Al-shebab daga birnin a shekara ta 2012, birnin da ke samar wa mayakan kudaden shiga domin sayen makamai.

Ko a shekara ta 2019, sai da mayakan suka kaddamar da makamancin wannan harin da ya kashe mutane 26 a Kismayu.

Har yanzu dai mayakan Al-Shebab ba su daddara ba a yunkurinsu na ganin sun kifar da gwamnatin Somalia domin kafa irin tasu gwamnatin, yayin da suka kashe dubban ‘yan kasar a jerin hare-haren da suka kaddamar cikin shekaru 10.

 

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 48 minutes 18 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 29 minutes 43 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com