Home DUNIYA Sojojin dake Mulki a Kasar Mali Sun Mayar da Rundunar ‘Yan Sandan...

Sojojin dake Mulki a Kasar Mali Sun Mayar da Rundunar ‘Yan Sandan Kasar Karkashin SU

Gwamnatin mulkin Sojin Mali ta mayar da ‘yan sandan kasar karkashin rundunar sojojinta, a kokarin da take yi na murkushe ‘yan ‘ta’adda masu ikirarin Jihadi, wadanda suka shafe shekaru akalla 10 suna addabar sassan kasar.

Gwamnatin sojin kasar ta Mali ta ce matakin zai ba ta damar jibge ‘yan sandan a yankunan da sojoji suka kwato daga hannun ‘yan ta’adda, domin tabbatar da tsaron jama’a da dukiyarsu, da kuma dakile duk wani yunkuri na masu ikirarin jihadi ko ‘yan tawaye sake mamaye yankunan da suka subuce musu.

Majalisar zartaswar kasar ta rikon kwarya ce kuma ta CNT wadda sojojin da suka yi juyin mulki suka kafa ta zartar da dokar baiwa jami’an tsaro na ‘yan sanda kayan aikin sojoji mako guda da ya gabata.

Sai dai tun kafin amincewa da aiwatar da matakin mayar da su karkashin rundunar sojoji kungiyoyin ‘yan sandan suka soki manufar da suka bayyana a matsayin shawarar da bangare daya yayi gaban kansa wajen zartaswa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp