Home DUNIYA An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020...

An Yiwa ‘Yan Jaridu 117 Kisan Gilla a Bakin Aikinsu daga 2020 zuwa 2021

Hukumar kula da ilimi, kimiyya al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO ta koka da yadda wani bincike ke nuna cewa kaso mai yawa na wadanda ke kashe ‘yan jaridu basa fuskantar hukunci kana bin da suka aikata.

Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Duniya ke bikin ranar kare hakkin ’yan jaridu, inda ta cikin rahoton da UNESCO ta fitar yau laraba, ta ce matsalar kisan ‘yan jaridu ta kai kololuwa a halin da ake ciki, yayinda kashi 86 na wadanda suka aikata kisan basa fuskantar hukunci.

Gabanin fitar da rahoton na yau, UNESCO a wani taron manema labarai da ta kira kan  barazanar da ‘yan jaridu ke fuskanta a sassan Duniya, ta bukaci daukar matakan baiwa ‘yan jaridun kariya la’akari da sadaukarwar da suke yi.

Rahoton na UNESCO ya ce wajibi daukar matakan gudanar da bincike tare da tabbatar da ganin an hukunta wadanda ke da hannu a cin zarafi ko kuma kisan ‘yan jaridu.

A cewar hukumar, halin da ‘yan jaridu ke ciki musamman a yankunan da ake fama da yaki ko kuma matsalolin tsaro baa bin yadda ba ne kuma ya na bukatar daukar matakan magancewa.

Manufar ranar ta yau na da nufin kare hakkin ‘yan jaridu tare da kawo karshen tsangwama ko kyara ko kuma cin zarafin da suke fuskanta a bakin aikinsu lamarin da UNESCO ta ce dole a samar da cikakkiyar kariya ga ‘yan jaridar.

Darakta Janar ta hukumar UNESCO Audrey Azoulay ta ce idan har ba a baiwa ‘yan jaridun kariyar da ta kamata ba, kenan za a dankwafar da hakkin fadar albarkacin baki.

Rahoton na UNESCO ya ce tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021 an yiwa ‘yan jaridu 117 kisan gilla lokacin da suke bakin aikinsu, yayinda wasu 91 kuma aka kashe ba a bakin aiki ba.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp