Ambaliyar Ruwa ta Hallaka mutane 9 a Afirka ta Kudu

Mutum tara sun mutu yayin da takwas suka ɓace sakamakon ambaliyar da wani kogi ya yi, inda ya tafi da masu bauta a wani coci.

Shaidu sun ce fiye da masu bauta 30 ne ke tsaye a kan duwatsun da ke kusa da kogin lokacin da ruwan mai gudun gaske ya ratso ta inda suke.

Shaidar ta ƙara da cewa an tsamo Faston da ke jagorantar ibadar bayan da ya maƙale cikin tarin bishiyoyin da ruwan ya taho da su.

Masu aikin ceto da suka haɗar da ‘yan sanda da jami’an kiyaye aukuwar bala’i na ci gaba da nemo waɗanda ruwan ya tafi da su.

Robert Mulaudzi mai magana da yawun ma’aikatar bayar da agajin gaggawa ta ƙasar ya ce sun samu gawa biyu ranar Asabar, tare da ceto mtum ɗaya wanda ya ce an kai shi asibiti domin kula da lafiyarsa.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 22 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 4 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com