Ma’aikatar Tsaron Jamhuriyyar Nijar ta tabbatar da Mutuwar Mutane 3 sakamakon Hadarin Jirgin Yaki

Wani jirgin soji mai saukar angulu kirar Mi-17, ya yi hadadi a filin sauka da tashin jiragen saman birnin Yamai da ke jamhuriyar Nijar, inda mutane uku da ke cikinsa suka rasa rayukansu nan take.

Ma’aikatar tsaron kasar ta ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 da mintuna 40 na safe.

Wata sanarwa da ma’aikatar da ma’aikatar tsaron kasar ta fitar a tsakiyar ranar litinin, ta ce jirgin ya yi hadari ne lokacin da yake sauka, bayan dawowa daga atisayen bayar da horo, kuma wadanda suka rasa rayukansu sun hadar da babban hafsan soji daya, da karamin hafsa daya sai kuma wanda ke horas da su dan asalin wata kasa ta kerare.

Ma’aikatar tsaron ta ce tuni ta kaddamar da bincike domin gano musababbin wannan hadari, tare da bayyana juyayi dangane da faruwar lamarin.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 16 minutes 1 second,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 57 minutes 26 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com