Gwamnatin Tarayyar Nijeriya tace Babu Batun Karin Albashin Ma’aikata

Gwamnatin Tarayya Nijeriya ta ce ba wani shiri da take yi na karawa ma’aikatan ta Albashi kamar yadda aka ruwaito a wasu jaridun kasar a kwanakin baya, inda ta ce wasu “alawus-alawus na musamman” ne kawai take shirin karawa.

Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Chris Ngige, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da kakakin ma’aikatar, Olajide Oshundun ya fitar, inda ya jaddada cewa babu batun sake yiwa ma’aikata karin Albashi.

Ngige, yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar gwamnati a ranar Talata, ya ce kwamitin da shugaban kasa ya kafa kan albashin ma’aikata na yin nazari, kuma ana sa ran zai fito da tsarin daidaita albashin a sabuwar shekara.

Sai dai ministan a ranar Juma’ar nan ya ce  karin da ya yi magana a kai shi kan alawus din wasu ma’aikatan na musamman ba wai karin Albashi ba, inda ya kara da cewa har yanzu ana kan aiki.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kwamitin shugaban kasa kan albashi (PCS) ta ofishin sakataren gwamnatin tarayya (OSGF) ya karbi shawarwarin duba alawus-alawus na ma’aikatu da hukumomin gwamnati da dama.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 14 hours 39 minutes 52 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 21 minutes 17 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com