Home General Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar DSS zata Tabbatar da tsaftataccen Zabe a 2023 – Afunanya

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta tabbatarwa da Al’ummar kasar
dana duniya baki daya tsayawa tsayin daka wajen ganin an gudanar databbatar da sahihin zabe a shekarar 2023.

Hukumar ta bayyana hakan ne ta cikin wata sanarwa da kakakin ta
Hukumar ta DSS Peter Afunanya, ya fitar, yayin da yake musanta rade-radin da ake yi na cewa hukumar tana gaban kotu tare da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta Mahmood Yakubu kan zargin kin bayyana kadarorin.

“Sanarwar tace, Hankalin hukumar ta DSS ya kai kan wallafar da wata jaridar yanar gizo tayi a ranar 5 ga watan
The statement said, “The attention of the Janairun 2023, wadda tace kuto ta dakatar da hukumar a kokarinta na kama shugaban hukumar zabe ta Kasar INEC.
“Hukumar ta gano cewa jaridar ta sauya ainihin abin da ya faru a kotun kuma ta ba da rahoton da bana gaskiya ba. Dangane da haka ne hukumar ta nuna rashin jin dadinta bisa abinda hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ya aikata. Abinda jaridar ta wallafa yasha bamban da kwafin shari’ar, ta kuma yi alkawarin gyarawa amma bata gyara ba.

“Wannan magana, duk da haka, ta zama mai mahimmanci domin fahimtar jama’a don fahimtar juna, musamman ma saboda rahoton karya da aka yada. Na cewa shugaban hukumar ya garzaya kotu.

“Duk da haka, hukumar tana sane da yadda wasu bata-gari ke son tada rikici a kasar, gami da haifar da cece-kuce game da babban zabe mai zuwa.
“Na daga cikin dabarunsu shine kawo cikas ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da lumana.

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja a ranar Laraba ta yi watsi da zarge-zargen bayyana kadarorin karya da ake yi wa Yakubu tare da hana jami’an tsaro gudanar da bincike a kansa.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp