Home General Ana cigaba da zaman makokin Jami’an Tsaron da ‘Yan Bindiga suka Hallaka...

Ana cigaba da zaman makokin Jami’an Tsaron da ‘Yan Bindiga suka Hallaka a jihar kaduna

A wani hari da ‘yan bindiga suka kai yankuna biyu na karamar hukumar Birnin Gwari na jihar Kaduna, ‘yan bindiga sun halaka jami’an tsaro da dama a yankin.

Rikicin ya samo asali ne, bayan jami’an tsaro sun kashe wani yaro makwanni uku da suka gabata, wanda yake kulawa ‘yan bindigan shanunsu.

Wannan ne ya sa ‘yan bindigar daukar fansa a ranar Litinin kan yankunan da mummunan lamarin ya auku na Kubau da Anguwan Zakara

‘Yan bindiga sun salwantar da rayukan jami’an tsaro da dama a yankuna biyu da inda suke cin karensu babu babbaka na karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, kamar yadda.

Daga cikin jami’an tsaron da suka rayukansu sun hada da; jami’an NSCDC, ‘yan sanda, soji da kuma wasu ‘yan sa kai a ranar Lahadi, kamar yadda majiyar ta bayyana.

“Ba ranar Lahadi bane suka fara harin, sai dai sun fara ne kwanaki hudu da suka wuce. An kai hari titin Funtua zuwa Birnin Gwari, inda jami’an tsaro da dama suka rasa rayukansu. Amma na ranar Lahadi, ‘yan sa kai biyu, ‘dan sanda daya da wani soja sun rasa rayukansu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp