Ana cigaba da zaman makokin Jami’an Tsaron da ‘Yan Bindiga suka Hallaka a jihar kaduna

A wani hari da ‘yan bindiga suka kai yankuna biyu na karamar hukumar Birnin Gwari na jihar Kaduna, ‘yan bindiga sun halaka jami’an tsaro da dama a yankin.

Rikicin ya samo asali ne, bayan jami’an tsaro sun kashe wani yaro makwanni uku da suka gabata, wanda yake kulawa ‘yan bindigan shanunsu.

Wannan ne ya sa ‘yan bindigar daukar fansa a ranar Litinin kan yankunan da mummunan lamarin ya auku na Kubau da Anguwan Zakara

‘Yan bindiga sun salwantar da rayukan jami’an tsaro da dama a yankuna biyu da inda suke cin karensu babu babbaka na karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, kamar yadda.

Daga cikin jami’an tsaron da suka rayukansu sun hada da; jami’an NSCDC, ‘yan sanda, soji da kuma wasu ‘yan sa kai a ranar Lahadi, kamar yadda majiyar ta bayyana.

“Ba ranar Lahadi bane suka fara harin, sai dai sun fara ne kwanaki hudu da suka wuce. An kai hari titin Funtua zuwa Birnin Gwari, inda jami’an tsaro da dama suka rasa rayukansu. Amma na ranar Lahadi, ‘yan sa kai biyu, ‘dan sanda daya da wani soja sun rasa rayukansu.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 28 minutes 7 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 9 minutes 32 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com