‘yan Bindiga sun sake sace dalibai a jihar Zamfara

‘Yan ta’adda a Najeriya sun kai hari kan dalibai mata na Kwalejin Lafiya da ke jihar Zamfara inda suka kwashe guda 4 bayan halartar wani bikin aure.

Bayanai daga yankin sun ce ‘yan ta’addar sun kama wadannan dalibai ne lokacin da suke komawa Kaura-Namoda daga Birnin Magaji bayan tare motocin da ke dauke da su inda suka kwashi matafiya 18, cikinsu har da daliban mata 4 da wasu ‘yan mata 3 da kuma wani mutum guda.

Tuni hukumomin Kwalejin Kula da Lafiyar ta hannun shugaban su Yusuf Maradun ya tabbatar da aukuwar lamarin wanda ya ce ba’a cikin makarantar aka kwashi daliban ba.

Maradun ya ce lokacin da aka sace wadannan daliban makarantar na hutun karshen shekara.

Wani ‘dan uwan daya daga cikin daliban ya ce ‘yan ta’addar sun bukaci diyyar Naira miliyan 20 kafin sakin diyarsu.

Jihar Zamfara na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro musamman hare- hare da kuma garkuwa da jama’a domin karbar kudin fansa.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 28 minutes 6 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 9 minutes 31 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com