Home General Hukumar ICPC ta kama Manajan Banki da Boye Sabon Kudi

Hukumar ICPC ta kama Manajan Banki da Boye Sabon Kudi

Hukumar yaƙi da laifukan cin hanci da rashawa a Najeriya, ICPC, ta kama manajan ayyuka na reshen bankin FCMB a Jihar Osun saboda zargin ɓoye sababbin takardun naira.

ICPC ta ce ta gano an zuba kuɗi a cikin na’urorin ATM na bankin amma a ɗaɗɗaure ta yadda ba za su iya fita ba idan mutane suka je cira, inda ta yi gargaɗi da a gyara.

“Sai dai da tawagar ta sake kai ziyarar duba a rana ta biyu, sai ta tarar ɗaya daga cikin ATM ɗin na ɗauke da ɗaurarrun kuɗin,” a cewar sanarwar da ICPC ta wallafa a shafukan zumunta.

Bisa wannan dalilin ne kuma jami’an hukumar suka tafi da manajan mai kula da ayyuka, wanda ba ta bayyana sunansa ba, na reshehn bankin na FCMB.

Haka nan, ICPC ta kama wata manajar bankin a Abuja “saboda ƙin saka kuɗi a ATM da gangan ko kuma sabo da mugunta duk da cewa akwai kuɗin,” in ji hukumar.

Jami’an tsaro da suka haɗa da na ‘yan sanda da EFCC na ci gaba da bin sawun bankuna da ɗaiɗaikun mutane don yaƙi da masu ɓoyewa da sayarwa da kuma yaɗa takardun jabu na sababbin kuɗin.

A gefe guda kuma, ‘yan Najeriya na ci gaba da kokawa kan ƙarancin kuɗin, inda suke shafe awanni a kan dogayen layuka don cirar su a na’urorin ATM.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp