Buhari na Jagorantar taron Majalisar Kolin kasar

Shugaba Buhari na jagorantar taron Majalisar Koli ta Kasa domin tattauna batutuwan da ke ci wa Najeriya tuwo a kwarya.
A na sa ran taron Majalisar da ke gudana a Fadar Shugaban Kasa zai tattauna kan matsalar mai, sauyin kudi, karancin takardun Naira da kuma sha’anin tsaro gabanin babban zabe da za a yi nan da mako biyu.
Taron ya samu halartar tsoffin shugabannin kasa irin su, Abdulsalami Abubakar, Goodluck Jonathan, Olusegun Obasanjo, da kuma Yakubu Gowon da gwamnoni da kuma Shugabannin Majalisar Dokoki ta Kasa.
Majalisar Koli ta Kasa wani bangare ne Gwamnatin Najeriya da ke ba da shawarwari kan tsare-tsaren gwamnati a bangaren zartaswa.
Mahalarta zaman na ranar Juma’a sun hada da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da Shugaban ’Yan Sandan Najeriya.
Haka kuma taron ya sami halartar Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya da sauransu.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 18 hours 31 minutes 15 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 20 hours 12 minutes 40 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com