Home General Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da...

Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da ake yaɗawa da sunan jami’anta ba

Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da ake yaɗawa da sunan jami’anta ba a shafukan sada zumunta.

Wannan na matsayin wani martani da ta mayar kan wasu rubuce-rubuce da ke yawo a shafukan sada zumunta, ta ce mutanen da ke kokarin haifar da ruɗani ke amfani da sunanta.

Babban Jami’in sadarwa na kasa a rundunar, Brigediya Janar Tukur Gusau, ya ce tuni sun kaddamar da bincike domin hukunta wadanda suka kirkiri wannan labari.

An dai rinƙa yawo da wasu bayanai kan rundunar da ke cewa, wasu daga cikin manyan jami’anta sun gana da daya daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa domin kawo rudani kan zaben da ake shirin gudanarwa nan da kwanaki goma sha uku masu zuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp