Home General A karo na 3 Buhari ya sake ganawa da Emefiele,

A karo na 3 Buhari ya sake ganawa da Emefiele,

Shugaba Nijeriya Muhammadu Buhari ya yi wata ganawar sirri da Gwamnan Babban Bankin kasar (CBN) Godwin Emefiele a fadarsa da ke Abuja.

Wannan shi ne karo na uku da gwamnan yake ganawa da shugaban tun bayan matsalar karancin takardar kudin kasar na naira da ta bullo a sakamakon sauyin wasu daga cikin manyan takardun kudin na 200 da 500 da kuma 1,000 da Babban Bankin ya yi.

Bayan wannan ganawar tasu ta uku a Aso Villa, Emefiele, ya ki cewa uffan ga manema labarai lokacin da ya fito.

Bugu da kari babu wata sanarwa daga fadar ko wani jami’i na gwamnati da ya bayyana dalilin ziyarar gwamnan bankin zuwa fadar shugaban kasar.

Sai dai duk da haka ana ganin ba za ta rasa nasaba da halin da kasar ke ciki ba na karancin takardun na naira da abin da wahalhalun da al’ummar kasar suka samu kansu a ciki a dalilin canjin.

Ko a ranar laraba da ta gabata shugaban kasar ya gana da gwamnan bankin bayan Kotun Kolin kasar ta dakatar da wa’adin da bankin ya sanya na daina karbar tsofaffin kudin daga ranar 10 ga watan Fabarairu.

Har sai Kotun ta yanke hukunci ranar Laraba da ke tafe, a kan karar da gwamnonin jihohi uku – na Kaduna da Kwara da kuma Zamfara suka shigar a kan batun canjin kudin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp