Home General Mutane 38 sun Mutu sakamakon cutar mashako ta (diphtheria) a jihar Kano

Mutane 38 sun Mutu sakamakon cutar mashako ta (diphtheria) a jihar Kano

Cibiyar yaki da cututtuka ta najeriya ta tabbatar da cewa mutum 216 ne cutar mashako (diphtheria) ta kama a jihohin Kano da Yobe da Lagos da kuma Osun.

Sannan kuma zuwa yanzu kamar yadda bayanan hukumar suka nuna cutar ta kashe mutum 40 a jihohin Kano da Lagos.

Daga cikin mutanen da suka rasu Kano tana da 38 yayin da Lagos take da biyu, in ji hukumar.

Haka kuma hukumar ta ce mutanen da suka kamu da rashin lafiya wadanda ake ganin ko cutar ce suma ta kama su yanzu sun kai 523 a jihohi biyar.

Jihohin kuwa su ne Kano da Yobe da Katsina da Lagos da kuma Osun.

Shugaban kwamitin kwararru da ke yaki da cutar ta mashako a hukumar ta NCDC, Dr Bola Lawal, shi ne ya gabatar da wadannan bayanai a wani taro ta intanet a jiya Litinin.

Dr Lawal ya ce hukumar ta tashi tsaye wajen taimaka wa kwararrun da ke aikin yaki da cutar a jihohin da ta bayyana na Kano da Katsina da Yobe da Lagos da kuma Osun.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp