Home General kotun majistare a jihar Kano ta aike da Alhassan Ado Duguwa...

kotun majistare a jihar Kano ta aike da Alhassan Ado Duguwa zuwa gidan gyaran hali

Wata kotun majistare a jihar Kano ta aike da shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Najeriya Alhassan Ado Duguwa zuwa gidan yari bayan gurfanar da shi a gaban kotun.
Ana zargin ɗan majalisar da muggan laifuka ciki har da zargin aikata kisan kai da mallakar makami ba bisa ƙa’ida ba da hannu a kunna wuta a wani gini wadda tayi sanadiyyar mutuwar wasu mutane tare da raunata wasu.
An gurfanar da shi gaban kotu mai lamba 54 dake No man’s land  tare da wani mutum wanda ake zargi sun haɗa baki wajen aikata kisan kai da tayar da zaune-tsaye a ƙaramar hukumar Tudun wada da ke jihar ranar Asabar da ta gabata.
Alƙalin kotun ya ɗage shari’ar zuwa ranar 7 ga watan Maris domin duba buƙatar yiyuwar bayar da belin ɗan majalisar ko kuma akasin haka.
Bayan fitowa daga kotun ne tashar PRNigeria ta sami zarafin tattaunawa da lauyan gwamnatin jihar kano Bar Lamido Abba Soron Dinki inda ya bayyana cewa yanzu haka za su yi Nazari kafin ranar da koton ta sanya a dawo domin cigaba da sauraren karar.
Shima a nasa bangaren lauyan dake kare wanda ake tuhuma Bar. Abdul Adamu Fagge ya bayyana dalilan da ya sanyasu bukatar kotun ta bayar da belin na Alhasan Ado Doguwa.
Akwai lauyoyin masu tarin yawa dake sanya idanu kan Shari’ar a karkashin Barista Mutari Dandago.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp