Kotu ta bayar da belin Alhassan Duguwa

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke jihar Kano, ta bayar da belin Alhassan Ado Duguwa.

Kakakin kotunan Kano, Baba Jibo Ibrahim ya ce hakan ya dace da tsarin shari’a, amma za a ci gaba da sauraron shari’ar zargin kisan kai da ake yi masa.

Ya ce Kotun ta kalubalanci rundunar ‘yan sanda saboda kai Alhassan Doguwa gabanta saboda ba ta da hurumin sauraron irin laifin da ake tuhumarsa da shi.

Yan sandan dai na kuma zargin sa da hannu a harbin wasu mutane da bindiga kwana ɗaya bayan kammala jefa ƙuri’a a mazaɓarsa ta Doguwa/Tudun wada a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya.

Ana kuma tuhumar ɗan majalisar da laifin kisan wasu mutum uku tare da raunata wasu guda takwas a ƙaramar hukumar Doguwa a lokacin da ake karɓa tare da bayyana sakamakon zaɓen ɗan majalisar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 50 minutes 7 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 31 minutes 32 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com