Home General Rundunar ‘Yan sandan Jihar kano ta zargi wasu da amfani da ‘yan...

Rundunar ‘Yan sandan Jihar kano ta zargi wasu da amfani da ‘yan Daba a zaben Gwamna dake tafe

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta ce ta samu bayanai da ke nuna cewa wasu ‘yan siyasa na shirin shigo da ‘yan bangar siyasa zuwa jihar domin tayar da hatsaniya a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki da ke tafe.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mamman Dauda shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, inda ya ce ‘yan siyasa da ke ganin za su fadi, tuni suka shirya tayar da tarzoma a zaɓen da ke tafe a ranar Asabar.

Sai dai, Mamman Dauda, ya gargaɗi dukkan ‘yan bangar siyasa da wasu ɓata gari cewa kada su kuskura su ta da fitina saboda a shirye ‘yan sanda suke wajen hukunta duk wanda aka kama da laifi.

CP Dauda ya kuma ce rundunar tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro a jihar za su tabbatar da cewa an kama dukkan waɗanda ake zargi, inda ya ce duk ɗan bangar siyasa da aka kama, za a tura shi zuwa kotu tare da waɗanda suka saka su aikin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp