Home DUNIYA Sama da yara dubu 500 na fama da tsananin yunwa a Yemen-UNICEF

Sama da yara dubu 500 na fama da tsananin yunwa a Yemen-UNICEF

Asususn tallafa wa kananan yara na majalisar dinkin duniya UNICEF yace akalla yara dubu 540 ne ke fama da matsanaciyar yunwa a Yemen, da rashin abinci mai gina jiki, wanda kuma ke barzana ga lafiyar su.

A cikin wani kundin bayani da asusun ya fitar, ya ce wannan matsala na kashe yaro guda cikin kowanne minti 10, a kasar da ke fama da tashin hankali.

Asusun na UNICEF ya kuma ci gaba da cewa bayan wadannan yara, akwai wasu guda miliyan 11 da ke neman tallafin gaggawa a kasar ta Yemen, inda kuma ake bukatar dala miliyan 488 a shekarar nan kadai don tallafa wa yaran.

Yakin da ake ci gaba da gwabzawa a kasar na ci gaba da taka rawa wajen jefa yaran cikin tashin hankali, tare da hana ma’aikatan jinkai shiga wasu yankunan don kai musu kayan tallafi, a cewar UNICEF.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp