Home SIYASA INEC ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe

INEC ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe a matsayin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Doguwa da Tudun Wada, daga Jihar Kano.

Karo na shida kenan, da Ɗan Majalisar na tarayya ke samun nasarar zuwa majalisar ta wakilai daga Jihar Kano, da ke Arewa Maso Yammacin Najeriya, tun bayan dawowar mulkin dimokraɗiyya a Najeriyar a cikin shekarar 1999.

Tun da farko dai hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙara (INEC) ta soke nasarar Da Hon. Alhassan Ado Doguwa ya samu, a zaɓen 25 ga watan Fabrairu, saboda jami’in sanar da sakamakon, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce “tursasa masa” aka yi.

Sai dai, jami’in sanar da sakamakon a zaɓen cike-giɓi na mazaɓar, Farfesa Sani Ibrahim a ranar 15 ga watan Afrilu, ya bayyana Alhassan Doguwa Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara da ƙuri’u 41,572 bayan wannan zaɓen lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp