Home DUNIYA Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Burkina Faso: Adadin mutanen da aka kashe a Karma ya kai 136

Wata kungiyar kare hakkin dan adam a Burkina Faso ta ce adadin fararen hula da aka kashe a kauyen Karma da ke yankin arewacin Burkina Faso a ranar 20 ga watan afrilun nan, ya kai 136, cikinsu akwai mata 50 da kananan yara 21.

Kididdigar da kungiyar ta fitar a ranar juma’a da ta gabata game da kisan ya kuma nuna jarirai 30, ‘yan kasa da wata 1 na daga cikin wadanda mayakan suka kashe.

Wasu ‘yan bindiga sanye da kayan soji ne suka farwa kauyen, inda  suka yi wa mutane da dama kisan gilla, harin da ke zuwa bayan wanda wasu mayaka masu ikirarin jihadi suka kai wani wuri kusan da kauyen Karma a ranar 15 ga watan Afrilun nan inda suka kashe sojoji 6 da wsu 34.

Kungiyar ta kuma ce baya ga wadannan, maharan sun kuma farwa wasu kauyuka na daban, inda suka kashe mutane 6 a kauyen Dinguiri, wasu 2 a Ménè, sannan suka kashe wasu mutanen 3 a kan hanyar dake tsakanin kauyukan Ouahigouya da Barga.

Adadin mamatan da alkalin Ouahigouya dake yankin arewacin kasar ya sanar a ranar lahadi na nuna kusan mutane 60 aka kashe a mabanbantan hare haren, saidai mazauna kauyen Karma da wasu shaidun gani da ido sun ce adadin ya zarce 100.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp