Home DUNIYA Jagoran adawar Kamaru John Fru Ndi ya mutu

Jagoran adawar Kamaru John Fru Ndi ya mutu

Rahotanni daga Kamaru na bayyana cewa Jagoran jam’iyyar adawar kasar ta SDF John Fru Ndi ya mutu a daren litinin ya na da shekaru 81 bayan fama da jinya.

Jagoran adawar shi ne dan siyasa mafi dadewa da ya ci gaba da zama a jam’iyyar adawa tun zuwan siyasar jam’iyyu da dama a kasar.

John wanda ya yi fama da doguwar jinya shi ne dan siyasa daya tilo da ya shafe tsawon lokaci ya na watsi da tayin shugaban kasar Paul Biya wanda ya nemi ya shiga cikin gwamnatin don tafiya tare.

John Fru Ndi ya shafe tsawon shekaru ya na caccakar salon kamun ludayin gwamnatin Paul Biya shugaban da ya shafe shekaru 38 ya na mulkar kasar ta gabashin Afrika.

Zuwa yanzu dai ba a sanar da lokacin gudanar da jana’izar jagoran adawar mai shekaru 81 ba, sai dai tuni ‘yan kasar suka fara makokinsa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp