Home DUNIYA ‘Yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci

‘Yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci

Wata sabuwar kididdiga ta duniya ta bayyana cewa, kimanin ‘yan Najeriya miliyan 71 na fama da bakin talauci, yayin da aka bayyana jihar Yobe a matsayin wadda ta fi fama da yunwa a kasar.

Tonye Cole, dan takarar gwamnan jihar Rivers karkashin jam’iyyar APC da ya gabatar da makala a wani taron ranar tunawa da yaki da yunwa ta duniya a birnin Abuja, ya bayyana cewa, wasu alkaluman Majalisar Dinkin Duniya sun ce, mutane dubu 25 ne ke mutuwa a kowacce rana sakamakon yunwa da suka hada da kananan yara dubu 10 a duniya.

Cole ya kuma bayyana cewa, Hukumar Kididdiga ta Najeriya ta kiyasta mutane miliyan 133 da ke fama da nau’uka daban-daban na yunwa a kasar.

Ya ce, ya zama dole Najeriya ta dauki mataki domin tunkarar wannan matsalar ta bakin talauci a Najeriya.

Kwararru sun ce akwai wasu dalilai da ke haddasa talauci a Najeriya kamar rikice-rikice da gurbatacciyar gwamnati da rashin ingancin tsarin kiwon lafiya da suka ce ya zama dole a magance su cikin gaggawa muddin ana son kawar da yunwa a kasar.

Jihar Yobe ce ta fi fama da matsalar yunwa a Najeriya, inda take da kashi 44.2, sannan jihar ce ke kan gaba taa fuskar samun matsalar rashin abinci mai gina jiki, inda a wannan bangaren take da maki 27.4 kamar yadda masana suka bayyana.

Sai kuma jihohin Zamfara da Kebbi da Jigawa da ke biye da Yobe wajen samun wannan matsalar ta fatara da yunwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp