Home General Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta Asibitocin PHCs a jihar

Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta Asibitocin PHCs a jihar

Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta asibitocin kiwon lafiya daga matakin farko na (PHCs) a wani yunkuri na inganta harkokin lafiya  a jihar da kuma inganta manyan asibitoci domin inganta bangaren lafiya.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Habu Dahiru, ne ya bayyana hakan yayi  da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya wato NAN a wata ziyarar gani da ido da kamfanin ya kai ranar alhamis.

Haka kuma kwamishinan ya kara da cewa a wani shirin hadin gwiwa da gwamnatin jihar tayi da Asusun tallafawa kananan yara na majalisar dinkin duniya, (UNICEF) wanda aka gyara asibitocin kiwon lafiya daga matakin farko (PHC) guda 114 domin kara karfafawa gami da inganta matakin lafiyar.

A cewar Mr. Dahiru, gwamnatin jihar na gudanar da aikin jinya don gano tare da tura ta tura yara masu fama da lalurar tamowa da mata masu juna biyu da ba basa samun damar zuwa asibiti domin haihuwa ta hanyar daukar matakai da dama.

Yace sama da ma’aikatan lafiya 600 da suka hadar da Ungozoma, ma’aikatan lafiyar al’umma, CHEW, aka tura zuwa asibitocin na matakin farko PHC a fadin kananan hukumomin jihar 11.

Daga bisani ya tabbatar da cewa daukar wannan mataki ya taimaka wajen rage yawan mutuwar nata masu juna biyu a fadin jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp