Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta Asibitocin PHCs a jihar

Gwamnatin jihar Gombe ta ce ta inganta asibitocin kiwon lafiya daga matakin farko na (PHCs) a wani yunkuri na inganta harkokin lafiya  a jihar da kuma inganta manyan asibitoci domin inganta bangaren lafiya.

Kwamishinan lafiya na jihar, Dr Habu Dahiru, ne ya bayyana hakan yayi  da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya wato NAN a wata ziyarar gani da ido da kamfanin ya kai ranar alhamis.

Haka kuma kwamishinan ya kara da cewa a wani shirin hadin gwiwa da gwamnatin jihar tayi da Asusun tallafawa kananan yara na majalisar dinkin duniya, (UNICEF) wanda aka gyara asibitocin kiwon lafiya daga matakin farko (PHC) guda 114 domin kara karfafawa gami da inganta matakin lafiyar.

A cewar Mr. Dahiru, gwamnatin jihar na gudanar da aikin jinya don gano tare da tura ta tura yara masu fama da lalurar tamowa da mata masu juna biyu da ba basa samun damar zuwa asibiti domin haihuwa ta hanyar daukar matakai da dama.

Yace sama da ma’aikatan lafiya 600 da suka hadar da Ungozoma, ma’aikatan lafiyar al’umma, CHEW, aka tura zuwa asibitocin na matakin farko PHC a fadin kananan hukumomin jihar 11.

Daga bisani ya tabbatar da cewa daukar wannan mataki ya taimaka wajen rage yawan mutuwar nata masu juna biyu a fadin jihar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 33 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 14 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com