Tinubu ya mika ta’aziyyasa ga AL’ummar Namibiya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya aike da saƙon ta’aziyyarsa ga al’ummar Namibiya bisa rasuwar shugaban ƙasar Hage Geingob.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale ya fitar, shugaba Tinubu ya ce ya kaɗu da jin labarin rasuwar mista Geingob, wanda ya bayyana da ɗan kishin gwagwarmayar tabbatar da dimokraɗiyya.

Shugaban na Najeriya ya kuma bayyana marigayin da jagoran tabbatar da jagoranci nagari, da bunƙasa tattalin arziki da ci gaba al’ummar Afirka.

Shugaba Tinubu ya ce marigayin ya rasu ne a daidai lokacin da nahiyar Afirka ke buƙatar jajirtattun shugabanni irinsa, waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen bunƙasa nahiyar ta ko wanne fannin ci gaba.

Daga ƙarshe shugaba Tinubu ya ce a madadin gwamnatinsa da al’ummar Najeriya suna miƙa saƙon ta’aziyyarsu ga ɗaukacin al’ummar Nambiya bisa wannan babban rashi da suka yi.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 22 minutes 16 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 3 minutes 41 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com