Fiye da mutum 40 sun mutu bayan fashewar madatsar ruwa a Kenya

Mutane da dama sun rasa rayukansu bayan fashewar wata madatsar ruwa a yankin Mai Mahiu da ke Kenya, kamar yadda ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta shaida wa BBC.

Gwamna a yankin, Susan Kihika ma ta tabbatar da mutuwar mutanen ga kamfanin dillancin labarai na AFP.

Ruwa ya ɓalle inda ya tafi da gidaje da motoci da dama a ƙauyen Kamuchiri sakamakon mamakon ruwan sama da ake yi a yankuna da dama na ƙasar.

Tawagar agaji na lalube cikin taɓo domin zaƙulo masu sauran numfashi, in ji kafafen yaɗa labaran ƙasar inda kuma suka yi gargaɗin adadin mutanen da suka mutu na iya ƙaruwa.

Lamarin ya datse babban titin da ya tashi daga Nairobi zuwa Mai Mahu bayan da manya-manyan duwatsu da taɓo suka rufe hanyar.

Tun farko, ƙungiyar agaji ta Kenya Red Cross ta ce ta kai mutane da dama zuwa asibiti a Mai Mahiu saboda ambaliya.

Adadin mutanen da suka mutu a yanzu sakamakon mamakon ruwan sama da ambaliya a ƙasar tun watan da ya gabata sun zarce 100.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 49 minutes 2 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 30 minutes 27 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com