Home General NAHCON ta kwashe Alhazai sama da Dubu 10 zuwa Saudiya

NAHCON ta kwashe Alhazai sama da Dubu 10 zuwa Saudiya

Hukumar Alhazai ta kasar nan ta ce kawo yanzu ta kwashe maniyyatan aikin hajjin bana 10,675 daga kasar zuwa kasa mai tsarki.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mataimakin daraktan harkokin yada labarai ta hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar, inda tace sun sami nasarar jigilar Maniyyata 4,665 ta jirgin FlyNas, sai jirgin Max Air da ya kwashe maniyyatan 4,479 jirgin Air Peace ya yi jigilar 1,531.

Ta kara da cewa kawo yanzu dai hukumar bata sami rahoton wani jirgi da aka soke tashin sa sai dai jirgin maniyatan jihar kwara da aka daga tashin sa a daren talata.

Haka kuma jihar Nassarawa ta zama jiha ta farko data fara kamala jigilar maniyyatan ta kimanin 1,794 na shekarar 2024 haka kuma jihar Oyo da rundunar sojoji ake sa ran zasu kamala jigilar zuwa dare.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp