Home General Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban NLC ya kammala ganawa da ƴansanda kan zargin ta’addanci

Shugaban ƙungiyar kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, bisa rakiyar ƴan ƙungiyar ƙwadago da Femi Falana, lauyoyi da suka haɗ da Femi Falana lauya mai rajin kare hakkin ɗanadam a Najeriya da Deji Adeyanju, ya gana da ƴansanda a hedikwatarsu da ke babban birnin tarayya domin amsa gayyatar suka yi masa.

Rundunar ‘yan sandan dai ta gayyaci shugaban NLC ɗin ne bisa zargin sa da tallafa wa ayyukan ta’addanci, wanda shugaban da ƙungiyar suka musanta.

Tun da karfe takwas na safe ne shugabannin NLC ɗin suka fara hallara a hedikwatarsu, inda suka gudanar da gangamin nuna hadin kai da goyon baya ga Ajaero.

Bidiyon da aka wallafa a shafin sada zumuntar NLC na X sun nuna wasu shugabannin kwadagon suna jawabi ga ma’aikatan da suka taru, wadanda suka tsaya kyam a bayan Shugaban nasu.

Kawo yanzu dai babu cikakken bayani na haƙiƙanin abin da ya faru a yayin ganawar.

Tun da farko dai ‘yan sandan sun gayyaci Ajaero a makon da ya gabata, bisa zargin bayar da kudade ga ayyukan ta’addanci, da cin amanar kasa, da kuma aikata laifuka ta shafukan sada zumunta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp