Home General Gwamnan Kano ya kwace kwangilar Titin Garko mai tsawon kilomi 5

Gwamnan Kano ya kwace kwangilar Titin Garko mai tsawon kilomi 5

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ziyarci Dam din Kafinchiri a karamar hukumar Garko, domin ganin yadda aiki ke gudana, wanda aka bayar da shi a yunkurin kawo sauyi a fannin noma a jihar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Lahadi.

Sanarwar tace aikin, wanda darajarsa ta kai Naira biliyan 2.5, an yi shi ne da nufin bunkasa noman rani da damina, da inganta samar da abinci, da kuma bunkasa tattalin arzikin jihar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada muhimmancin aikin noman na Kafinchiri, inda ya bayyana hakan a matsayin wani muhimmin bangare na kokarin gwamnatinsa na bunkasa noma a jihar Kano.

Ya bukaci mazauna garin Garko da kewaye da su yi amfani da damar da aikin zai bayar domin inganta tattalin arzikin su da jihar baki daya.

A wani labarin kuma, Gwamnan ya sanar da kwace kwangilar aikin hanyar karamar hukumar Garko mai tsawon kilomita biyar saboda gazawar dan kwangilar na dawowa bakin aiki.

Ya ba da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba za a baiwa wani mai kwazo kwangilar aikin don tabbatar da kammala aikin a kan kari.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma kuduri aniyar samar da cibiyar lafiya ta zamani a garin Garko, da nufin kusantar da harkokin kiwon lafiya ga jama’a.

Ya nuna jin dadinsa bisa goyon bayan da al’ummar yankin suke ba shi tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba gudanar da aiyukan cigaba a jihar .

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp