Home General Mun dakile hari kan kayan hukumar DSS – Sojojin Najeriya

Mun dakile hari kan kayan hukumar DSS – Sojojin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar da cewa ta daƙile yunƙurin ƴan ta’adda a Jihar Neja daga kai hari a kan kadarorin Hukumar DSS.

Wata majiyar tsaro ta shaida wa PRNigeria cewa sojojin, da taimakon jirgin Super Tucano na sojojin sama sun yi nasarar kashe wasu ƴan ta’addan da suka kai harin.

Majiyar wadda ta nemi a ɓoye sunanta ta ce lamarin ya faru ne a garin Bassa a ƙaramar hukumar Shiroro na jihar.

A cewar majiyar, sojojin sun samu nasara a kan ƴan ta’adda bayan samun bayanan sirri a kan shirinsu na kai harin a kan kayayyakin DSS.

“Nan da nan aka tashi jiragen Super Tucano, inda suka samu nasarar daƙile yunƙurin na ƴan bindigan. Sannan harin jirgin ya kashe aƙalla ƴan bindiga 30,” inji majiyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp