Ambaliya- Al’ummar Maiduguri na ci gaba da karbar tallafi

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bai wa mutanen da ambaliyar Maiduguri ta shafa tallafin dala miliyan shida.

Wata sanarwa da ofishin jami’in kula da ayyukan jin kai a Najeriya, Mohammed Fall ya fitar, ya ce haɗin gwiwar ƙungiyoyin agaji na MDD da masu zaman kansu, ciki har da Red Cross, sun kai ziyara birnin Maiduguri a karshen mako.

A cewarsa, tawagar ta haɗu da mutanen da abin ya shafa – waɗanda yawanci rikicin Boko Haram da kuma rashin tsaro ya riga ya ɗaiɗaita.

“Mu tare da haɗin gwiwar wasu ƙungiyoyi na samar wa da mutanen kayan abinci, muna kuma jefa musu abinci ta sama a wuraren da ke wahalar kai wa, har ma da ruwan sha,” in ji shi

Ya kuma ce suna kula da lafiyar waɗanda aka tsugunar a sansanoni musamman ma mata da yara mata da kuma tabbatar da cewa ba a samu ɓarkewar cutuka ba.

Ambaliyar ta afku ne bayan fashewar madatsar ruwa ta Alau wanda ke nisan kilomita goma da kudancin Maiduguri.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 31 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 13 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com