NLC ta sanya wa kamfanonin Layin waya sharudda a Nijeriya

Kungiyar ƙwadago ta Najeriya, NLC ta nemi kamfanonin sadarwar da ke aiki a kasar su janye sabon farashin su kuma koma wa tsohon farashi cikin gaggawa.

A wata takardar bayan taro da ƙungiyar ta fitar wanda ta gudanar ranar Talatar nan a birnin Lokoja na jihar Kogi, NLC ta ɗauki wasu matakai guda bakwai kan al’amarin kamar haka:

  • Janye ƙarin farashin da komawa tsohon farashi har zuwa lokacin da kwamitin da ƙungiyar ta kafa ya kammala gudanar da bincike.
  • Ƙungiyar ta buƙaci ma’aikatan Najeriya da sauran ƴan ƙasa da su ƙaurace wa kiran waya ko amfani da datar kamfanonin MTN da Airtel da Glo a kowacce rana daga ƙarfe 11:00 na safe zuwa ƙarfe 2:00 na rana na kowace rana har zuwa ƙarshen watan Fabrairu.
  • Ta umarci ƴan Najeriya da su daina sayen data daga kamfanonin
  • Ƙungiyar na buƙatar kamfanonin su dawo wa Najeriya da kuɗaɗen da suka kwashewa ƴan ƙasar
  • Ƙungiyar za ta jagoranci rufe ayyukan kamfanonin ranar 1 ga watan Maris idan dai har ba su janye sabon ƙarin da suka yi ba ya zuwa ƙarshen watan Fabrairu.
  • Ƙungiyar ta umarci dukkannin rassanta na jihohi da su zaburar da mambobinsu gabanin 1 ga watan na Maris.
  • Ƙungiyar ta umarci dukkan sauran sassanta da su ja hankalin mambobinsu wajen ƙaurace wa kira ko amfani da datar kamfanoni a sa’o’in da aka ayyana

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1464 days 10 hours 59 minutes 49 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1446 days 12 hours 41 minutes 14 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com